MAKANCEWAR TINIBU
Jinkirta Jana'iza Ba Zai Tayar da Matattu Ba: Darasin Jonathan da Makancewar Tinubu BARR SOLOMON DARLUNG Babu wani shugaban kasa a tarihin Najeriya da ya samu goyon bayan neman tazarce kamar Goodluck Jonathan. 'Yan siyasa daga kowane bangare, gwamnoni, sanatoci, sarakunan gargajiya, shugabannin addinai, attajirai, da sama da kungiyoyin goyon baya 10,000 masu karfi da kudi sun mamaye kafafen watsa labarai kullum, suna tabbatar da nasararsa—wasu har kafin karfe 12 na rana a ranar zabe. A zamanin gwamnatin Jonathan, kudi ba matsala ba ce. Ana wulwula su babu tunani, duk wanda ya nuna goyon baya yana samu. Har abin ya kai, kawai ka gaishe “Mama Peace” da “Ina kwana,” za ka samu ruwan kudi. Wata guda kafin zaben Fabrairu 2015, gwamnatin Jonathan ta boye ta dauko kwararren mai binciken ra’ayi daga kasa da kasa domin tantance sakamakon zabe. Abin mamaki, binciken ya nuna cewa idan aka gudanar da zabe a lokacin da aka tsara, Jonathan zai fadi. A gigice, shugaban ya kira NSA Sambo Dasu...